Ezekiyel 48:1-7
1
“Ga kabilan, a jere bisa ga sunayensu. “A iyaka ta arewa, Dan zai sami rabo; zai bi hanyar Hetlon zuwa Lebo Hamat. Hazar-Enan da iyakar arewancin Damaskus kusa da Hamat za tă zama sashen iyakarsa a wajen gabas zuwa wajen yamma.
2
Asher zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Dan daga gabas zuwa yamma.
3
Naftali zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Asher daga gabas zuwa yamma.
4
Manasse zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Naftali daga gabas zuwa yamma.
5
Efraim zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Manasse daga gabas zuwa yamma.
6
Ruben zai sami rabo; zai yi iyaka da Efraim daga gabas zuwa yamma.
7
Yahuda zai sami rabo; zai yi iyaka da yankin Ruben daga gabas zuwa yamma.
Settings