Skip to content
Ezekiyel 43:1-6

Ezekiyel 43:1-6

1
Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
2
sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
3
Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
4
Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
5
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
6
Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options