Ezekiyel 23:1-4
1
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2
“Ɗan mutum, an yi mata biyu, ’yan matan mahaifiya guda.
3
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi ’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
Settings