Skip to content
Fitowa 21:12-17

Fitowa 21:12-17

12
“Duk wanda ya bugi mutum har ya kashe shi, lalle a kashe shi.
13
Amma in ba da nufin yă kashe shi ba, sai dai in Allah ne ya nufa haka, to, sai mutumin yă tsere zuwa inda zan nuna muku.
14
Amma in mutumin ya yi dabara har ya kashe wani mutum da gangan, sai a ɗauke shi daga bagadena a kashe shi.
15
“Duk wanda ya bugi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
16
“Duk wanda ya saci mutum ya sayar da shi, ko kuwa aka iske shi a hannunsa, lalle kashe shi za a yi.
17
“Duk wanda ya la’anta mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options