Skip to content
Afisawa 5:21-25

Afisawa 5:21-25

21
Ku yi biyayya da juna saboda bangirmar da kuke nuna wa Kiristi.
22
Matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, kamar ga Ubangiji ne kuke yi.
23
Gama miji shi ne kan mace, yadda Kiristi yake kai da kuma Mai Ceton ikkilisiya, wadda take jikinsa.
24
To, kamar yadda ikkilisiya take biyayya ga Kiristi, haka ma ya kamata mata su yi biyayya ga mazansu cikin kome.
25
Maza, ku ƙaunaci matanku, kamar yadda Kiristi ya ƙaunaci ikkilisiya, ya kuma ba da kansa dominta.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options