Skip to content
Daniyel 5:25-31

Daniyel 5:25-31

25
“Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
26
“Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
27
“Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
28
“Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
29
Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
30
A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
31
Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options