Ayyukan Manzanni 20:32-38
32
“To, yanzu na danƙa ku ga Allah da kuma ga maganar alherinsa, wadda za tă iya gina ku ta kuma ba ku gādo a cikin dukan waɗanda aka tsarkake.
33
Ban yi ƙyashin azurfa ko zinariya ko tufafin kowa ba.
34
Ku kanku kun san cewa hannuwan nan nawa sun biya mini bukatuna da kuma na abokan aikina.
35
Cikin kowane abin da na yi, na nuna muku cewa da irin wannan aiki tuƙuru don mu taimaki marasa ƙarfi, muna tunawa da kalmomin da Ubangiji Yesu kansa ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’ ”
36
Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a.
37
Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba.
38
Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.
Settings