Tsallake zuwa abun ciki
Ayyukan Manzanni 15:36-41

Bulus da Barnaba Sun Rabu

Ayyukan Manzanni 15:36-41
36
Bayan ’yan kwanaki sai Bulus ya ce wa Barnabas, “Mu koma mu ziyarci ’yan’uwa a duk garuruwan da muka yi wa’azin bisharar Ubangiji mu ga yadda suke.”
37
Barnabas ya so Yohanna, wanda ake kira Markus ya tafi tare da su,
38
amma Bulus bai ga ya kyautu ya tafi da shi ba, domin ya yashe su a Famfiliya bai kuwa ci gaba tare da su a aikin ba.
39
Suka sami saɓanin ra’ayi tsakaninsu har suka rabu. Barnabas ya ɗauki Markus suka shiga jirgin ruwa zuwa Saifurus,
40
amma Bulus ya zaɓi Sila suka kuwa tashi, bayan ’yan’uwa suka danƙa su ga alherin Ubangiji.
41
Ya ratsa ta Suriya da Silisiya, yana ƙarfafa ikkilisiyoyi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options