Tsallake zuwa abun ciki
2 Sama’ila 14:21-24

Absalom Ya Koma Urushalima

2 Sama’ila 14:21-24
21
Sarki ya ce wa Yowab, “To, da kyau, zan yi haka. Je ka, ka dawo da saurayin nan Absalom.”
22
Yowab ya rusuna har ƙasa don bangirma, ya kuma yi wa sarki kyakkyawar fata. Yowab ya ce, “Yau, bawanka ya sani ya sami tagomashi a gare ka, ranka yă daɗe sarki, gama sarki ya ji roƙon bawansa.”
23
Sa’an nan Yowab ya tafi Geshur ya dawo da Absalom Urushalima.
24
Amma sarki ya ce, “Yă tafi gidansa; kada yă zo yă gan ni.” Saboda haka Absalom ya tafi gidansa, bai kuwa je ganin sarki ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options