Skip to content
2 Sarakuna 10:25-28

2 Sarakuna 10:25-28

25
Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
26
suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
27
Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
28
Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options