Skip to content
1 Sama’ila 19:11-14

1 Sama’ila 19:11-14

11
Shawulu ya aiki mutane zuwa gidan Dawuda su yi gadin gidan, su kuma kashe Dawuda. Amma Mikal matar Dawuda ta gargaɗe Dawuda, ta ce, “In ba ka gudu a daren nan ba, kashegari za a kashe ka.”
12
Haka kuwa Mikal ta sauko da Dawuda ta taga ya gudu, ya tsere.
13
Sai Mikal ta ɗauki gunki ta kwantar da shi a gādo, ta sa masa gashin akuya a kansa, sai ta rufe da mayafi.
14
Da Shawulu ya aiki mutane su kama Dawuda. Mikal ta ce, “Ba shi da lafiya.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options