1 Sama’ila 1:12-14
12
Yayinda take addu’a ga Ubangiji, Eli ya lura da bakinta.
13
Hannatu tana addu’a a zuci, ba a jin muryarta, sai leɓunanta ne kawai suna motsi. Eli kuwa ya yi tsammani ta bugu ne.
14
Sai ya ce mata, “Har yaushe za ki ci gaba da maye? Ki daina shan ruwan inabi.”