Skip to content
1 Sarakuna 9:15-19

1 Sarakuna 9:15-19

15
Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
16
(Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga ’yarsa, matar Solomon.
17
Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
18
da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
19
Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options