Skip to content
1 Korintiyawa 9:1-5

1 Korintiyawa 9:1-5

1
Ba ni da ’yanci ne? Ni ba manzo ba ne? Ni ban gan Yesu Ubangijinmu ba ne? Ba ku ne sakamakon aikina cikin Ubangiji ba?
2
Ko da waɗansu ba su ɗauke ni a matsayin manzo ba, tabbatacce, ni manzo ne a gare ku! Gama ku ne hatimin manzancina a gaban Ubangiji.
3
Wannan ita ce kāriyata ga waɗanda suke tuhumata game da manzancina.
4
Ba mu da ’yancin ci da sha ne?
5
Ba mu da ’yancin tafiya tare da matar da muka aura mai bi kamar sauran manzanni da ’yan’uwan Ubangiji da kuma Kefas suke yi?
Settings

Reading style

Typeface

Font size 19px

Reading width 90 chars

Options