Skip to content
1 Korintiyawa 9:1-6

1 Korintiyawa 9:1-6

1
Ba ni da ’yanci ne? Ni ba manzo ba ne? Ni ban gan Yesu Ubangijinmu ba ne? Ba ku ne sakamakon aikina cikin Ubangiji ba?
2
Ko da waɗansu ba su ɗauke ni a matsayin manzo ba, tabbatacce, ni manzo ne a gare ku! Gama ku ne hatimin manzancina a gaban Ubangiji.
3
Wannan ita ce kāriyata ga waɗanda suke tuhumata game da manzancina.
4
Ba mu da ’yancin ci da sha ne?
5
Ba mu da ’yancin tafiya tare da matar da muka aura mai bi kamar sauran manzanni da ’yan’uwan Ubangiji da kuma Kefas suke yi?
6
Ko ni da Barnabas ne kawai ba mu da ’yanci a ɗauke mana aikin ci da kai?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options