Skip to content
1 Korintiyawa 15:5-10

1 Korintiyawa 15:5-10

5
cewa ya bayyana ga Bitrus, sa’an nan ga Sha Biyun.
6
Bayan haka, ya bayyana ga fiye da ɗari biyar daga cikin ’yan’uwa a lokaci guda. Yawancinsu kuwa suna nan da rai, ko da yake waɗansu sun riga sun yi barci.
7
Sa’an nan ya bayyana ga Yaƙub, sa’an nan ga dukan manzannin,
8
a ƙarshe duka, ya bayyana a gare ni, kamar wanda an haifa a lokacin da bai kamata ba.
9
Gama ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban kuma isa a kira ni manzo ba, domin na tsananta wa ikkilisiyar Allah.
10
Amma bisa ga alherin Allah, na zama abin da nake, alherinsa zuwa gare ni kuwa bai zama a banza ba. A’a, na yi aiki fiye da dukansu, duk da haka, ba ni ba ne, sai dai alherin Allah da yake tare da ni ne.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options