Skip to content
1 Korintiyawa 15:12-20

1 Korintiyawa 15:12-20

12
Amma in ana wa’azi cewa Kiristi ya tashi daga matattu, yaya waɗansu a cikinku suke cewa babu tashin matattu?
13
In babu tashin matattu, to, ba a tā da Kiristi ma ba ke nan.
14
In ba a tashe Kiristi ba kuwa, ai, wa’azinmu, da bangaskiyarku banza ne.
15
Sai ma ya zama mun zama masu ba da shaidar ƙarya game da Allah ke nan, domin mun shaida game da Allah cewa ya tashe Kiristi daga matattu. Bai tashe Kiristi ba ke nan, in lalle ba a tā da matattu.
16
Gama in ba a tā da matattu ba, to, Kiristi ma ba a tashe shi ba ke nan.
17
In kuwa ba a tashe Kiristi ba, bangaskiyarku a banza take, ya zama har yanzu kuna cikin zunubanku ke nan.
18
Ashe, waɗanda suka yi barci a cikin Kiristi ma sun hallaka ke nan.
19
In a wannan rayuwar ce kaɗai muke da bege cikin Kiristi, mun zama abin tausayi fiye da dukan mutane.
20
Amma tabbatacce, an tā da Kiristi daga matattu, nunan fari kuwa cikin waɗanda suka yi barci.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options