Skip to content
1 Tarihi 12:8-15

1 Tarihi 12:8-15

8
Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
9
Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
10
Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
11
Attai na shida, Eliyel na bakwai,
12
Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
13
Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
14
Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
15
Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options