Zabura123
Listen to this chapter
0:00
0:00
1
Waƙar haurawa. Na tā da idanuna gare ka, gare ka da kursiyinka yake cikin sama.
2
Kamar yadda idanun bayi suna duban hannun maigidansu, kamar yadda idanun baiwa suna duban hannun uwargijiyarta, haka idanunmu suna duban Ubangiji Allahnmu, sai ya nuna mana jinƙansa.
3
Ka yi mana jinƙai, ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai, gama mun jimre da reni mai yawa.
4
Mun jimre da wulaƙanci daga masu girman kai, reni mai yawa daga masu fariya.
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Options
Study Note