Skip to content
Zefaniya 1:1-3

Zefaniya 1:1-3

1
Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options