Romawa 3:9-19
9
To, me za mu ce ke nan? Mun fi su ke nan? Ina, ko kaɗan! Mun riga mun zartar cewa da Yahudawa da Al’ummai duk suna a ƙarƙarshin zunubi.
10
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Babu wani mai adalci, babu ko ɗaya;
11
babu wani mai fahimta, babu wani mai neman Allah.
12
Duk sun kauce gaba ɗaya, sun zama marasa amfani; babu wani mai aikata nagarta, babu ko ɗaya.”
13
“Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗun kaburbura ne, harsunansu suna yin ƙarya.” “Dafin mugun maciji yana a leɓunansu.”
14
“Bakunansu sun cike da la’ana da ɗacin rai.”
15
“Ƙafafunsu suna saurin kai su zuwa ga zub da jini;
16
hallaka da baƙin ciki suna ko’ina a hanyoyinsu,
17
ba su kuma san hanyar salama ba.”
18
“Babu tsoron Allah a idanunsu.”
19
Yanzu mun san cewa dukan abin da doka ta ce, tana magana ne ga waɗanda suke ƙarƙarshin doka, saboda a rufe kowane baki; dukan duniya kuma ta ba da lissafin kanta a gaban Allah.
Settings