Ru’uya ta Yohanna 2:25-29
25
Sai dai ku riƙe abin da kuke da shi har sai na zo.’
26
Gare shi wanda ya ci nasara ya kuma aikata nufina har ƙarshe, zan ba shi iko a kan al’ummai.
27
‘Zai yi mulki a kansu da sandar sarauta ta ƙarfe, zai farfashe su, kamar tukwanen yumɓu’kamar yadda na karɓi iko daga Ubana.
28
Zan kuma ba shi tauraron asubahi.
29
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.
Settings