Zabura 89:9-11
9
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.