Tsallake zuwa abun ciki
Zabura 78:67-72

Allah ya zaɓi Yahuda, Sihiyona da Dawuda

Zabura 78:67-72
67
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options