Zabura 78:26-31
26
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
Settings