Skip to content
Zabura 78:23-28

Zabura 78:23-28

23
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options