Skip to content
Zabura 77:14-20

Zabura 77:14-20

14
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. Sela
16
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options