Skip to content
Zabura 73:4-12

Zabura 73:4-12

4
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na ’yan adam.
6
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options