Zabura 71:1-3
1
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.