Zabura 70:1-3
1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
2
Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
3
Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
Settings