Skip to content
Zabura 70:1

Zabura 70:1

Ana nuna aya 1 tare da mahallin da ke kewaye.
1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
2
Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
3
Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
4
Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options