Skip to content
Zabura 69:19-28

Zabura 69:19-28

19
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options