Skip to content
Zabura 64:3-6

Zabura 64:3-6

3
Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
4
Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
5
Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
6
Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options