Zabura 59:6-10
6
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
7
Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8
Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
9
Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
10
Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
Settings