Skip to content
Zabura 56:9-13

Zabura 56:9-13

9
Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
10
Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
11
ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
12
Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
13
Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options