Skip to content
Zabura 55:16-23

Zabura 55:16-23

16
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, Sela mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options