Zabura 49:6-10
6
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Settings