Zabura 37:12-15
12
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
Settings