Skip to content
Zabura 33:13-18

Zabura 33:13-18

13
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan ’yan adam;
14
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,

Nazarin nassin nan

Sharhi a kan nassin, ba aya ɗaya ba

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • 1 Bitrus 3:12

    Gama idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kunnuwansa kuma suna jin addu’arsu, amma fuskar Ubangiji tana gāba da masu mugunta.”
    daga aya ta 18
  • Ayuba 36:7

    Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
    daga aya ta 18
  • Zabura 147:11

    Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
    daga aya ta 18
  • Zabura 34:15

    Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
    daga aya ta 18
  • Zabura 34:20

    yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
    daga aya ta 18
  • Ayuba 28:24

    Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
    daga aya ta 13
  • Karin Magana 21:31

    Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.
    daga aya ta 17
  • Ibraniyawa 6:18

    Allah ba ya karya! Haka ma alkawuransa da rantsuwarsa abubuwa biyu ne da ba a iya canjawa. Mun gudu zuwa wurin Allah domin kāriya. Ya kamata alkawuransa su ƙarfafawa sosai mu riƙe begen nan da yake gabanmu.
    daga aya ta 18
  • Zabura 11:4

    Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon ’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
    daga aya ta 13
  • Irmiya 32:19

    manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
    daga aya ta 15
  • Zabura 20:7

    Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
    daga aya ta 17
  • Zabura 13:5

    Amma na dogara a kan ƙaunarka marar ƙarewa; zuciyata tana farin ciki a cikin cetonka.
    daga aya ta 18
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options