Ubangiji yana lura da mutanensa
12
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan ’yan adam;
14
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Settings