ข้ามไปยังเนื้อหา
Zabura 33:12-22

Zabura 33:12-22

12
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan ’yan adam;
14
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options