Skip to content
Zabura 31:14-18

Zabura 31:14-18

14
Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
15
Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
16
Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
17
Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari.
18
Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options