Zabura 28:6-9
6
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
7
Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
8
Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
9
Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.
Settings