Skip to content
Zabura 22:22-25

Zabura 22:22-25

22
Zan furta sunanka ga ’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options