Skip to content
Zabura 22:12-21

Zabura 22:12-21

12
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options