Skip to content
Zabura 139:1-12

Zabura 139:1-12

1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
2
Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
3
Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
4
Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
5
Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
6
Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
7
Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
8
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can.
9
In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
10
can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
11
In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
12
duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options