Zabura 136:10-24
10
Gare shi wanda ya kashe ’ya’yan fari Masar Ƙaunarsa madawwamiya ce.
11
Ya kuma fitar da Isra’ila daga cikinsu Ƙaunarsa madawwamiya ce.
12
Da hannu mai ƙarfi da hannu mai iko; Ƙaunarsa madawwamiya ce.
13
Gare shi wanda ya raba Jan Teku biyu Ƙaunarsa madawwamiya ce.
14
Ya kawo Isra’ila ta tsakiyarsa, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
15
Amma ya share Fir’auna da mayaƙansa cikin Jan Teku; Ƙaunarsa madawwamiya ce.
16
Gare shi wanda ya bi da mutanensa cikin hamada, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
17
Wanda ya buge manyan sarakuna, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
18
Ya karkashe manyan sarakuna, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
19
Sihon sarkin Amoriyawa Ƙaunarsa madawwamiya ce.
20
Da kuma Og sarkin Bashan, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
21
Ya kuma ba da ƙasarsu gādo, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
22
Gādo ga bawansa Isra’ila; Ƙaunarsa madawwamiya ce.
23
Shi wanda ya tuna da mu cikin ƙasƙancinmu Ƙaunarsa madawwamiya ce.
24
Ya kuma ’yantar da mu daga abokan gābanmu, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
Settings