Zabura 130:1-4
1
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.