6
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8
Saboda ’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.