Zabura 121:1-4
1
Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
2
Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
3
Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
4
tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
Settings